ABNA24 : Wannan ne yasa musulmin kasar Faransa suka janye gudanar da bukukuwan maulidin manzon Allah da suka shirya, domin yin alhinin abin da ya faru, tare da fitar da bayanai da ke yin tir da hakan, da kuma tabbatar da cewa duk wanda ya aikata baya wakiltarsu a matsayinsu na musulmin kasar Faransa.
Duk da irin wannan matsaya da musulmin kasar Faransa suka dauka da ma sauran musulmi na duniya da ke yin tir da abin da faru, da kuma nisanta haka da mahnaga ta addinin muslunci, amma shugaban kasar ta Faransa Emmanuel Macron ya sake maimata kalamansa na sukar addinin musl;unci, tare da bayyana abin da ya faru da cewa ta’addanci ne na musulunci.
Kafin wannan lokaci dai al’ummomin musulmi sun nuna bacin ransu da kalaman da ya yi makamanta hakan, a cikin ‘yan kwanakin da suka gataba, inda yake kokarin nuna cewa aikin ta’addanci yana damfare ne da akidar addinin muslunci.
342/